Advertising
Advertising
Labarai

Zazafan martanin Sheikh Khalid bayan saukeshi daga limancin masallaci.

Babban Limamin Masallacin Juma’a na unguwar ’yan majalisu ta Apo da ke Abuja, wanda aka dakatar, Sheikh Nuru Khalid, ya mayar da martani kan dakatarwar da aka yi masa, saboda hudubar da ya yi wacce bisa alama ba ta yi wa gwamnati dadi ba.

Advertising

A ranar Asabar ce Kwamitin Masallacin, karkashin jagorancin Sanata Sa’idu Dansadau, ya sanar da dakatar da malamin daga limanci, saboda kalamansa a hudubarsa ta sallar Juma’a kan matsalar tsaro, musamman harin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna.

Sheikh Khalid, a cikin martanin nasa dai, ya wallafa wata ayar Alkur’ani, inda ya rubuta: “Allah Shi ne mafi girma. Shi ke ba da mulki ga wanda Ya so, kuma Ya kwace daga wanda Ya so.”

Hakan dai na zuwa ne ’yan sa’o’i bayan dakatar da shi daga limancin, inda ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da addu’a.

Advertising

“Ya Allah, Kai ne mai girma da daukaka, Kai ke ba da mulki ga wanda Ka so, Ka kwace daga wanda Ka so, Ka daukaka wanda Ka so, kuma Ka kaskantar da wanda Ka so. Dukkan alheri a hannunKa yake, Kai ne mai iko a kan komai,” kamar yadda ya wallafa ayar.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button