Advertising
Advertising
Labarai

Wata Matar aure ta bayyana dalilin da yasa take zuwa wajan wani dan bindiga yake lalata da ita

Wata Matar aure wanda take kai wa kanta wajan wani dan bindiga yana lalata da ita ta bayyana cewa, taan aikata hakan ne domin kada a kashe iyayan ta.

Advertising

Matar wanda mazauniya ce a wani kauye mau suna Tankarau dake yankin Madaci a karamar hujumar Zariya dake Jihar Kaduna, ta bayyana sunan dan bindigar da yake lalatar da ita inda tace sunan sa Idi Dan Ibrahim.

Matar ta bayyana hakan ne a lokacin da aka kamata kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Sannan Matar ta bayyana cewa: Tun da nake zuwa wajen dan bindigar ya yi lalata dani sau daya ya taba bani N5,000 daga baya kuma idan naje bana yarda da shi, sai dai ince mishi bani da lafiya ko ina jini don haka sai ya daina bani komai.

Advertising

Bayan haka Matar ta kara da cewa: Ta shiga damuwa sosai lokacin da aka kamata sabida yadda Mijin ta da ‘Iyayan ta suka shiga damuwa, sabida ganin halin da take ciki.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button