Advertising
Advertising
Labarai

Wata sabuwar Amarya ta bukaci a raba Auren su da Angon ta sabida Mazakutar sa ta mata girma domin tana shan wahala lokacin Jima’i

Wata sabuwar Amarya ta nemi koyu ta raba Auren su da Angon data Aura bayan sati biyu 2 da yin Auren nasu, sabida ta bayyana yadda take shan wahala a duk lokacin da suke Jima’i.

Advertising

Al’amari ya faru ne a wata Kotu a Samaru dake Gusau a Jihar Zamfara inda Amaryar ta bayyana Kotun cewa, Angon nata yana yawan bukatar yin Jima’i da ita sai dai kuma Mazakutar sa ta mata girma.

Ai’sha wato Amaryar ta bayyana cewa: A daren farkon da Angon nata ya fara saduwa da ita mai makon taji dadi amma sai take shan wahala sabida Mazakutar Angon nata babba ce.

Sanna ta kara da cewa: A rana ta biyu 2 da suka sake yin Jima’i da Angon nata sai al’amarin ya sake kazanta inda wahalar da take sha ta nunku akan ta baya, inda tace a nan ne tasan bazata iya jurewa ba.

Advertising

Amma daga karshe Angon ta bayyana cewa: Ya yarda da bukatar da matar sa ta fada na raba Auren su, inda yace ya amince a raba Auren nasu kamar yadda ta nema.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button