Advertising
Advertising
Labaran Kannywood

Kungiyar matan kannywood zasuyi karar Naziru Sarkin waka idan bai janye kalaman daya fada akan su ba

Kungiyar matan kannywood zasuyi karar Naziru Sarkin waka idan bai janye kalaman daya fada akan su ba

Sakin layin da Naziru M Ahmad ya yi wanda aka fi sani da Sarkin waka akan ‘yan kannywood kan maganar lalata da ‘yam mata kafin a sanya su a shirin fim, wannan maganar ta janyo masa cece-kuce da maganganu kala-kala.

Advertising

Bayan jarumai da Daraktotin masana’antar sun sha tofa albarkacin bakin su kan maganar da Sarkin waka ya fada akan su, to a yanzu kuma jarumai mata na masana’antar kannywood sun yi gangami domin daukar mataki akan maganar da Sarkin waka ya fada akan su.

A yau ne wani rahoton takarda ya fito daga shugabancin Hauwa A Bello kan maganar da Naziru Sarkin waka ya fada a kan su na sai anyi lalata da su ake sanya su a shirin fim.

Wanda maganganun da Sarkin waka ya fada sun tada kura a masana’antar kannywood bayan Ladin Cima tayi shira da BBC Hausa, har ta bayyana musu kudin da ake bata a harkar tasu ta fim inda tace ma ba’a taba bata sama da dubu biyu ko uku ko biyar ba.

Advertising

To a yau kuma shine kungiyar matan kannywood Association suka fitar da wata takarda zuwa ga Naziru M Ahmad wato Sarkin waka, inda takardar take cewa.

Assalamu alaikum,
Kungiyar matan ‘yan kannywood women association of nigeria (k-wen) karkashin jagorancin shugabancin ni shugabar kungiyar a madadin yan kungiya.

Duba da abin da ya faru wanda naziru M Ahmad yayi wasu kalamai na chin zarafi ga mata masu sana’ar fim muna kira a gare shi da ya janje kalamansa cikin kwana ukku da yau in kuwa bai yi haka ba zamu kaishi kotun musulunci bisa tuhumar yayi mana kazafi.

Nagode.

Hauwa A Bello.

Shugaba.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button