Matar aure ta saka ‘yan daba sun sace ‘yar Adama matar Kamaye sun yayyanketa sabida tana soyayya da Mijin ta
Wani labari da Zahra’u Sale da aka fi sani da Adama ta shirin Dadin Kowa ko adamar kamaye ta kawo a shafinta na TikTok ya taba zuciya na yadda gidan radion Premier dake kano suka kawo wani rahoto da ya bayyana.
Wata matar aure da kawar ta sun dauko hayar ‘yan daba sun dauke Faiza ja’afar wadda ya’ ce ga Adaman suka tafi da ita wani kango suka
yayyanke ta da ja mata kunne ta rabu da mijin matar.
An dai yi nasarar kama matar auren da kawar ta da da kuma biyu daga ‘yan daban yayin da ita kuma Fa’iza ya’ ga Adaman take kwance a gadon Asibiti tana samun kulawa daga raunukan da suka yi mata.
Adama ta wallafa wannan Rahotona shafinta natiktok gami da rubuta ku tayani jaje inda cikin
rahoton wakilin gidsn radion ya samu zantawa da Fa’iza da Mijin matar da kuma ita Adaman.
Ga bidiyon zantawar tasu a kasa domin ku kalla.