Advertising
Advertising
Labarai

Yadda sojojin Nigeriya suka shirya Gasar rawa daomin tabbatar da zaman lafiya a kasar.

Rundunar (OPSH) a Filato ta shirya gasar raye-rayen al’adu don inganta zaman lafiya a tsakanin kabilu daban-daban a Karamar Hukumar Barkin Ladi Plateau.

Advertising

Ishaku Takwa, mai magana da yawun rundunar, a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi a cikin Jos, ya ce an gudanar da taron ne a ranar Asabar a Barkin Ladi.

Da yake jawabi a wajen taron, kwamandan rundunar, Ibrahim Ali, ya ce gasar na daga cikin hanyoyi wajen samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Mista Ali ya ce sojoji za su ci gaba da daukar dabaru daban-daban wajen tabbatar da zaman lafiya don tabbatar da kwanciyar hankali ya dawo a dukkan sassan Filato.

Advertising

“Bari in yi amfani da wannan damar don sanya Al’ummar Filato su yi amfani da al’adunsu masu dimbin yawa wajen inganta hadin kai da zaman lafiya a tsakanin kabilu daban-daban na jihar.

Babu wata mafita da ta wuce zaman lafiya kuma kyawun zaman lafiya shine lokacin da mutane suka taru don yin bikin tare ba nuna bambancin al’adunsu,” in ji shi.

Mista Ali ya bukaci jama’a da su ba jami’an tsaro hadin kai da goyon baya domin samun dauwamammen zaman lafiya da tsaro a cikin al’umma.

Ya kuma shawarci mazauna Filato da su guji duk wani nau’in tashin hankali, su kuma koyi zaman lafiya da makwabta.

Mungode da bibiyar shafinmu kucigaba da kasancewa damu dan samun zagagan labarai.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button