Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya baiwa Abdussamad, Dantata da Dangote Mulki
Yanzu-yanzu muka sami labarin gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya nada Aminu Dantata, Aliko Dangote da kuma Abdussamad Isyaku Rabiu, a matsayin mambobi na kwamitin gudanarwa na Hukumar Zakka da Hubusi ta jihar Kano.
Kwamishinan yada labarai na jihar Muhammad Garba shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, inda yake cewa Dakta Ibrahim Muazzam Maibushira shi ne a ka nada a matsayin Shugaban kwamitin.
Kamar yadda Kwamishinan yace, sun hada da Dakta AbdulMutallab Ahmed a matsayin Kwamishina I, sai kuma Dakta Lawi Sheikh Atiq a matsayin Kwamishina na ll a hukumar.
Bayan haka kuma akwai sauran wanda sun hada da wakilan Masarautar jihar Kano, wakilan Ma’aikatar Yada Labarai, Wakilan Ma’aikatar Harkokin Addinai, sai na kasuwannin kurmi, Rimi, Kwari da Singa.