Advertising
Advertising
Labaran Kannywood

Daga kune Lalacewar Tarbiyyar yara ba daga fina fina Hausa ba Jaruma Nafisat Abdullahi.

Daga kune Lalacewar Tarbiyyar yara ba daga fina fina Hausa ba Jaruma Nafisat Abdullahi.

Advertising

Shahararriyar jarumar nan ta masana’antar finafinan Kannywood, Nafisa Abdullahi tayi kalamai masu kaushi akan mutanen dake sukar finafinan Hausa.

Nafisa Abdullahi a wani rubutu da tayi a shafin ta na Twitter tace ko kaɗan finafinan Hausa ba sa ɓata tarbiyyar yara sai dai idan dama can asali yaran ba su samu tarbiyya a gida ba.

“Ba yadda za a yi mutane su bar yaran su na kallon finanfinan ƙasar Amurka (Hollywood), finafinan Indiya (Bollywood) dana kudancin Najeriya (Nollywood), sannan su buɗe baki suce finafinan Hausa ne ke ɓata tarbiyyarsu.” Inji ta

Mutane da dama dai na ganin cewa finafinan Hausa na wannan zamanin na zama wani abin gurɓata tarbiyyar yara, musamman yadda ake nuna wasu abubuwan da suka ci karo da al’adar Hausawa.

Advertising

An sha korafi akan yadda masana’antar ta koma nuna wasu abubuwa waɗanda suka ci karo da ɗabi’a da al’adar Hausawa, sai dai jarumar na ganin cewa masana’antar bata ɓata tarbiyya.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button