Advertising
Advertising
Labaran Kannywood

Fina finan mu basa bata tarbiyyar cewar jarumar Kannywood Nafisa Abdullahi.

Tsohuwar jaruma a masana’antar finafinan Kannywood, Nafisa Abdullahi tayi kalamai masu kaushi akan mutanen dake sukar finafinan Kannywood.

Advertising

Jaruma Nafisa Abdullahi tayi wani rubutu a kafar sada zumunta ta Twitter ida ta bayyana rashin jituwa n dadinta a game da masu cewa finafinai Hausa na lalata tarbiyyar yara.

Mutane da dama dai na ganin cewa finafinan Hausa na wannan zamanin na zama wani abin gurɓata tarbiyyar yara, musamman yadda ake nuna wasu abubuwan da suka ci karo da al’adar Hausawa.

A rubutun da jarumar tayi ta bayyana cewa ba yadda za a yi mutane su bar yaran su na kallon finanfinan Hollywood, Bollywood dana kudancin Nollywood, sannan su buɗe baki suce finafinan Hausa ne ke ɓata tarbiyya.

Advertising

Ga kalaman da jarumar ta wallafa a shafin nata na twitter.

Kuna kallon finafinan Hollywood, finafinan Bollywood da finafinan turanci na Najeriya, sannan ku zo ku ce finafinan Hausa ke ɓata tarbiyya… haba? Kuna barin yaran ku su kalla, suna amfani da wayoyi da yanar gizo, amma…. finafinan Hausa ke lalata tarbiyya. Ba su da tarbiyya dama tun farko.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button