Advertising
Advertising
Labarai

Ina neman afuwar al’ummar Nageriya akan wakar da nayiwa shugaba Buhari kafin ya hau mulki, cewar Ibrahim Yala

Ficaccan mawakin nan Ibrahim Yala Hayin Banki wanda ya rera wakar yau Nageriya riko sai mai gaskiya Baba Buhari kai muke so Nageriya.

Advertising

Ya bayyana a cikin wata bidiyo inda yake neman afuwar al’umma Nageriya da su yafe masa, sannan kuma yana mai shidawa al’umma cewa zai yi wasu wakoki wanda zasu warware kalaman da ya yiwa shugaba Muhammad Buhari.

Ga dai cikekkiyar sanar war tasa a kasa.

Salamu Alaikum Warahmatullah. Ina Mai sanar da masu bibiya ta a kafar sadarwa ta zamani cewa. Ni Ibrahim Yala Hayin Banki (Mai Bakandamiyar wakar Buhari wacce na Sanya ta a wannan post din danayi. Zan saki sababbin
wakoki na guda biyu idan Allah Ya kaimu 1-1-2022 Insha Allah. Wakokin sune: Yan Nigeria ku yafemin da Kuma Taron tsintsiya Babu shara.

Advertising

Sannan kuma ga wata bidiyon sanarwar tasa nan a kasa domin ku kalla kuji mai yake fada.

Advertising

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button