Advertising
Advertising
Labaran Kannywood

Babban bakin ciki na a rayuwa shine saida Allah ya daukaka ni sannan mahaifiyata ta mutu, cewar mawaki Namenj

Shahararran mawakin hausa mai tashe a yanzu wato, Namenj, ya bayyana wani al’amari a shafin sa na sada zumunta Instagram wanda jama’a suka tausaya masa, kamar yadda yayi wallafar tasa kamar haka.

Advertising

Mawaki Namenj yace: Mama na ta rasu kafin na sami daukaka kuna nasan addu’arta ne ya kaini inda nake a yanzu, Allah yajikan mahaifiyata Hajiya Fatima da rahama.

Bayan wannan damuwar tasa mawaki Namenj ya mika godiya ga masoyansa da kuma sanannun mutane wanda suka taimaka masa suka nuna masa kauna.

Sanannun mutanen da mawaki Namenj yake fadin cewa sun taimaka masa da nuna masa kauna ba wasu boyayyu bane kowa ya sansu sune kamar haka, Hadiza gabon, Ali nuhu, Abdullahi nuhu, MR EAZI, Kannywood da dai sauran su.

Advertising

Sannan kuma mawaki Namenj ya fidda sabbin sabon kuddin wakokin sa mai suna North Star, wato tauraron Arewa yana nan yana zaga Duniya.

https://www.instagram.com/p/CWFsP_SKLku/?utm_medium=copy_link

Advertising

One Comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button