Masha Allah: Jarumin Fina Finan Kudancin Nigeria Jim Iyke Ya Karɓi Addinin Musulunci
Daga Aliyu A Tsiga
Fitaccen jarumin fina-finan Nollywood na Najeriya, Jim Iyke, ya bayyana cewa ya bar addinin Kiristanci kuma ya Musulunta. A cewarsa ya yanke shawarar ne bayan karanta littafai daya zurfafa da kuma fayyace abubuwa da dama.
Hakan na zuwa ne bayan da ya bayyana yadda ya haɗu da wata mata musulma a kwanan baya inda ya bayyana hakan saboda bambancin addini. Fitaccen jarumin a cikin faifan bidiyon ya yi kira da a kawar da ra’ayin addini, yana mai cewa mutane da dama na ci gaba da fuskantarsa har yau.
Ya ƙara da cewa mutane na iya zama tare cikin lumana duk da bambancin ra’ayi na rayuwa, addini, siyasa da dai sauransu.
Muna rokon Allah ya dauwamar dashi cikin wannan addini da babu kamar sa ya kuma kara karkato kan sauran kafurai da su gane gaskiya.
Mungode da bibayar shafin mu a ko da yaushe, Ku cigaba da Kasancewa damu dan samun zafafan labara.
Babban tatsuniya. Labari mara tushe, karya tsantsa.
Toh, shi da Kansa ya karyata. Don Allah a dai na yada karya.